Kyaftin kasar Belgium Eden Hazard ya sanar da yin murabus daga bugawa kasar sa wasa.
Hazard ya bayyana haka ne a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta Instagram a wannan rana ta Laraba.
Dan wasan wanda ke wasa a Real Madrid ta kasar Sifaniya, ana kallon matakin na da alaka da ficewa tin a matakin rukuni da kasar ta Belgium tayi a gasar kofin duniya ta shekarar 2022 da ke gudana a Qatar.
Eden Hazard ya buga wasa 126 da cin kwallo 33 a duka fafata da yayiwa kasar sa.
“Kwarai Ina godiya gareku matuka, bisa goyan baya da Kuma fatan alkhairi da kuka nuna min, a cewar Hazard a sakon da ya wallafa a shafinsa na Instagram.
Ya ce ya dauki matakin ne domin samun hutu da kuma bawa wasu damar da suma zasu nuna bajintarsu.
Mai shekara 31 Hazard tin a shekarar 2008 ya fara bugawa Belgium wasa, sai dai har kawo yanzu babu wani kofi da ya lashe a matakin kasar ta Belgium.