Saurari premier Radio
25.1 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiSojoji sun sake ceto daya daga cikin 'yan matan Chikbok

Sojoji sun sake ceto daya daga cikin ‘yan matan Chikbok

Date:

Rundunar sojin kasar nan ta ceto daya daga cikin ‘yan matan Chikbok.

Rundunar sojin kasar nan a Talatar nan ta gano wata mai suna Mary Ngoshe, daya daga cikin ‘yan matan makarantar sakandire ta Chibok da Boko Haram suka a shekarar 2014.

Rundunar ta gano tane rike da jariri wanda ake zargin nata ne yayin da suke sunturi a yankin Ngoshe na jihar Borno.

Wannan na kunshene cikin wata sanarwa da rundunar sojin kasar nan ta fitar a shafinta na Twitter a safiyar Laraba.

“Rundunar soji ta 26 yayin sunturi a yankin Ngoshe a jihar Borno ta gano wata mai suna Mary Ngoshe wacce daya ce daga cikin ‘yan matan makarantar sakandire ta Chibok ta aka sace a shekarar 2014”, a wallafar Twitter ta rundunar.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...