Majalisar dokokin jihar Kano ta karbi kwarya kwaryar kasafin kudi na naira biliyan 58 daga gwamnan kano Abba Kabir Yusif.
Shugaban majalisar Isma’il Falgore ne ya bayyana karbar kasafin a jiya litinin, inda yace gwamnatin jihar na neman sahalewar majalisar kamar yadda sashe na 121 karamin sashe na A da B cikin baka na kundin tsarin mulki 1999 ya tanada.
Falgore yace gwamnatin tace aiwatar da kasafin a yanzu ya zama wajibi domin saita alkiblar ayyukan gwamnati wajen cimma burin da ta sa gaba na gabatar da muhimman ayyuka a wanna shekara.
An dage zaman majalisar zuwa yau Talata domin cigaba da tattauna batun.