Saurari premier Radio
39.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMajalisa zata tantance sabbin kwamishinonin da Ganduje zai nada a ranar Litinin

Majalisa zata tantance sabbin kwamishinonin da Ganduje zai nada a ranar Litinin

Date:

Majalisar dokokin Kano zata tantance sabbin kwamishinonin da gwamnatin Kano ta aike mata a ranar Litinin 22 ga watan Agustan da muke ciki.

Gwamantin Kano ta aike da sunayen sabbin kwamishinonin kuma ‘yan majalisar zartaswar ne domin maye gurbin wadanda suka ajiye aiki don yin takara a matakai daban daban.

 

Shugaban majalisar Injiniya Hamisu Ibrahim Chidari, ne ya karanta sunayen sabbin kwamishinonin a zaman majalisar na yau Litinin.

 

Wakilin mu Aminu Abdullahi Ibrahim ya ruwaito cewa cikin wadanda za a nada akwai

 

1) Garba Yusuf Abubakar tsohon kwamishinan kudi zamanin gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau.

 

Majalisar dokokin Kano za tayi bincike akan Kano Pillars

2) Lamin Sani Zawiyya.

 

3) Ibrahim Dan Azumi Gwarzo.

 

4) Abdulhamid Abdullahi Liman.

 

5) Ya’u Abdullahi ‘Yan Shana.

6) Yusif Jibril Rurum.

 

7) Adamu Abdu Fanda.

8) Saleh Kausani.

Majalisar ta kuma gayyaci mutanen takwas domin tantance su a ranar Litinin 22 ga watan da muke ciki na Agusta don nadasu kwamishinonin a ma’aikatu daban daban.

Latest stories

Related stories