Saurari premier Radio
27.6 C
Kano
Tuesday, April 30, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKiwon LafiyaLikitoci na gargadi kan shan ruwan gishiri da siga barkatai a watan...

Likitoci na gargadi kan shan ruwan gishiri da siga barkatai a watan Azumi

Date:

Karibullah Abdulhamid Namadobi

Masana kiwon lafiya na gargadi ga al’umma game da amfani da sinadarin ruwan gishiri da suga a wannan lokaci na azumin watan Ramadan ba tare da amincewar likita ba.

Hakan ya biyo bayan wasu al’umma ke amfani da sinadarin a Lokutan buda baki da sahur barkatai ba tare da shawrar likita ba.

A zantawar wakilinmu Ahmad Adamu Yau da wani likita da ke jihar Yobe, Dakta Isma’il Hashim, ya ce wannan shan ruwan gishi da suga ba tare da umarnin likita ba, ya kan haifar da matsala.

Dakta Isma’il Hashim ya ce mutukar mutum ya na shan ruwan gishi da suga ba tare da shawarar likita ba, hakan ka iya haifar da cutar hawan jini da sauran cutuka.

Dakta Isma’il Shanono ya bukaci al’umma dasu kasance suna tu’ammali da abubuwa bisa shawarwarin masana domin gujewa kamuwa da cuta.

Wasu mazauna Kano sun bayyana cewa, suna amfani da sinadarin a matsayin wani abu da zai kara kuzari bayan kwashe tsawon lokaci ana ibadar azumi.

Latest stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...

Related stories

Ƙungiyar Hamas ta isa birnin Al-Qahira game da tattaunawa kan tsagaita wuta.

Rahotanni daga kasar Masar, sun ce tawagar jami’an kungiyar...

An kashe ƴan ƙato da gora sama da 23 a Barno da Sakkwato.

Rahotanni daga jihohin Borno da Sakkwato sun ce, an...