Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC zasu tsunduma yajin aiki bayan da suka baiwa gwamnatin kwanaki 14 da zasu fara, kuma wa’adin zai fara daga gobe 9 ga wata Fabarairu.
Sun zargi gwamnatin tarayyar da rashin aiwatar da yarjejeniya 16 da aka kulla tsakaninsu da gwamnatin tarayya.
Shugabannin kungiyoyin NLC da TUC sun bayyana damuwarsu da cewa, duk da kokarin da kungiyoyin kwadago ke yi na inganta zaman lafiya a ma’aikatu, ga dukkan alamu gwamnati ba ta damu da wahalhalun da al’umma suke ciki ba.
Kungiyar NLC da TUC sun ce da Zarar wa’adin ya cika nan da kwanaki 14 zasu tsunduma yajin aiki.