Wani kamfanin fito na ƙasar Denmark, A.P. Moller-Maersk, ya amince wajen zuba jarin kudi dala milyan dari shida a tashoshin jiragen ruwan kasar nan.
Kamfanin ya ayyana aniyar zuba jarin ne yayin ganawar da shugaba Bola Tinubu ya yi da shugabansa, Robert Maersk Uggla, a gefen taron kasuwanci na duniya da aka gudanar a birnin Riyadh na Saudiyya.
Shugaba Tinubu, ya ce jarin da kamfanin zai zuba zai ƙarfafa dala milyan dubu ɗaya da tuni aka sanya domin inganta tashoshin jiragen ruwa a gabashi da yammacin kasar nan.
Gwamnatin tarayya dai ta yi alƙawarin inganta tashoshin jiragen ruwanta, ciki har da waɗanda ke birnin Lagos, cibiyar kasuwancin ƙasar nan, domin sauƙaƙa harkokin cinikayya