Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif ya dakatar da Manajan Daraktan kamfanin samar da Aikin Gona na Kano (KASCO) Dakta Tukur Dayyabu Minjibir.
Sanarwar dakatarwar na dauke da sahannun sakataren Gwamnatin Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi, wanda sakataren yada Labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar.
Dakatar da manajan daraktan nada alaka da zarginsa da hannu a sayar da hatsin da bai dace ba na Gwamnatin Jihar Kano.
Sanarwar tuni ta umarci Dakataccen Dayyabu da ya mika al’amuran kamfanin ga babban jami’in maaikatar.