Gwamnan Kano Ganduje, ya dage rantsar da sabin kwamishinoni a Larabar nan tare da jajantawa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa da wadanda gini ya fado musu a kasuwar saida wayoyi ta Beirut.
Cikin sanarwar da kwamishinan yada labarai Muhammad Garba, ya fitar gwamna Abdullahi Umar Gamduje, ya jajantawa wadanda al’amarin ya shafa tare da bada umarnin ci gaba da bincike don kubutar da wadanda suka makale a ginin da ya rushe.
Ya bada tabbacin ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin rugujewar ginin yayin da ake tsakiyar ginawa.
‘Yan sanda a Kebbi sun kama matar da ta kashe mijinta
Cikin sanarwar Ganduje ya kuma yi alhini ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a sassa daban daban na jihar nan.