Saurari premier Radio
31.9 C
Kano
Friday, April 26, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai'Yan sanda a Kebbi sun kama matar da ta kashe mijinta

‘Yan sanda a Kebbi sun kama matar da ta kashe mijinta

Date:

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kebbi ta kama wata mata da ake zargi da kashe tsohon mijinta.

Tsohon mijin mata alƙalin kotun majistare ne mai suna Attahiru Ibrahim Zagga.

Kakakin rundunar, SP Nafiu Abubakar, ya shaidawq manema labarai cewa da misalin ƙarfe 9:00 na dare ranar Alhamis ne maƙota suka kai musu rahoton cewa sun ji hayaniya a gidan alƙalin da ke unguwar Alieru a birnin Kebbi.

Da isar jami’ansu ne kuma suka tarar da Attahiru kwance cikin jini, inda suka garzaya da shi asibita kuma a can ne likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

“Bayan shigar jami’anmu gidan suka tarar da tsohuwar matarsa mai suna Farida Abubakar kuma aka kama ta da zargin hannunta a aikata kisan,” in ji SP Nafiu.

Kafin mutuwarsa, Attahiru Ibrahim alƙalin kotun majistare ne a garin Jega na Ƙaramar Hukumar Jega.

Latest stories

Related stories