Manoman albasa a jihar Kano sun ce farashin albasa ba zai yi saukar da ake tunani ba a bana duba da tsadar man fetur wanda da shi ne suke amfani domin injinan ban ruwa.
A zantawar sa da wakiliyarmu Hafsat Iliyasu Dambo, sakataren kungiyar manoman albasa na kasa reshen Kano, Mustafa Adamu, ya ce ko da farshin zai sauka to ba zai wuce da kashi 2 cikin 100 na farshinta na yanzu ba.
Yace suna hasahen albasar za ta kuma yi karanci sakamakon tsadar man fetur a kasar nan, domin da shi injinan ban ruwa ke amfani.
Mustafa Adamu, ya ce a tarihi ba a taba samun hauhawar farashin albasa kamar bana ba.
Al’umma musamman ma mata na ci gaba da kokawa sakamakon tashin farshin albasa wanda suke ganin kuma ita ce jigo wajen girki.