Saurari premier Radio
40.5 C
Kano
Sunday, May 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniFA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a...

FA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a wasan karshe

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ,zata fafata da Manchester City a wasan karshe na gasar cin kofin kalubale na kasar Ingila FA Cup.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Man United tayi nasarar doke Brighton da ci 7-6 a bugun daga kai sai mai tsaran gida a ranar Lahadi.

Ita kuwa Man City tin a ranar Asabar ta lallasa Shefield United da ci 3-0 a wasan da suka fafata.

Yanzu haka dai a karon farko a wasan karshe a gasar FA Cup, Man City da Man United zasu kece raini da juna a gasar ta kakar wasannin shekarar 2022/2023.

Kuma ana saran wasan karshen zai gudana a ranar Uku ga watan Yunin bana, kuma babban filin wasan kasar Ingila Wembley ne zai karbi bakuncin wasan.

Latest stories

Atiku yace lokaci ya yi da za a yanke shawarar ko zai kara tsayawa takarar shugaban kasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, yace magoya bayan...

Related stories

Kano Pillars ta dakatar da mai horas da ƴan wasanta nan take.

Hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta...

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...