Saurari premier Radio
25.6 C
Kano
Friday, July 26, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniFA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a...

FA Cup:Man City da Man United zasu kece raini da juna a wasan karshe

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ,zata fafata da Manchester City a wasan karshe na gasar cin kofin kalubale na kasar Ingila FA Cup.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Man United tayi nasarar doke Brighton da ci 7-6 a bugun daga kai sai mai tsaran gida a ranar Lahadi.

Ita kuwa Man City tin a ranar Asabar ta lallasa Shefield United da ci 3-0 a wasan da suka fafata.

Yanzu haka dai a karon farko a wasan karshe a gasar FA Cup, Man City da Man United zasu kece raini da juna a gasar ta kakar wasannin shekarar 2022/2023.

Kuma ana saran wasan karshen zai gudana a ranar Uku ga watan Yunin bana, kuma babban filin wasan kasar Ingila Wembley ne zai karbi bakuncin wasan.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories