Saurari premier Radio
24.5 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniMan City ta koma matakin farko a Teburin gasar Firimiyar Ingila

Man City ta koma matakin farko a Teburin gasar Firimiyar Ingila

Date:

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, ta koma matakin farko a gasar Firimiya ta kasar Ingila bayan doke Fulham da ci 2-1.

Nasarar da Manchester City tayi, hakan ya kuma bawa Dan wasa Erling Haaland damar zura kwallo 50 a duka kakar wasanni ta bana.

Haaland ne ya fara zura kwallon farko a bugun daga Kai sai mai tsaran gida a minti na 3, sai kuma dan wasa Carlos Vinicius ya warware kwallon a minti na 16.

Sai dai kuma dan wasa Julian Álvarez ya sanya kwallo ta biyu ga Man City a minti na 36 bayan samun taimakon Riyard Mahrez.

Yanzu haka Dan kasar Norway Halland, ya zamo a gaba-gaba a yawan zura kwallo a gasar Firimiya ta Ingila.

Wanda hakan ke nuna ya kusa kamo Andy Cole da ya zura 34 lokacin ya na Newcastle a kakar 1993-94, kana shima Alan Shearer ya nuna irin bajintar lokacin yana Blackburn a shekarar data biyo baya.

Kawo yanzu Manchester City ta koma saman Arsenal da tazarar maki daya.

Kuma hakan shi ne na farko da Manchester City ta koma saman Arsenal a tsakiyar kakar wasanni, wajen yunkurin lashe gasar Firimiya da Champions League da kuma FA Cup.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories