Gwamnatin jihar Jigawa ta ayyana Juma’ar nan a matsayin ranar hutu don taya jihar murnar cika shekaru 31 da kirkirarta.
Arsenal zata fafata da Crystal Palace a wasan farko na gasar Firimiya
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Isma’il Ibrahim, ya fitar a Alhamis din nan.
Gwamnatin jihar ta kuma yabawa al’ummar jihar tare da bukatar suyiwa jihar addu’a da kasa baki daya.
An dai kirkiri jihar Jigawa daga Kano a ranar 27 ga watan Agustan shekarar 1991 lokacin mulkin soji karkashin Ibrahim Babangida.
A yanzu dai jihar nada kananan hukumomi 27.