Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Tuesday, April 23, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniArsenal zata fafata da Crystal Palace a wasan farko na gasar Firimiya

Arsenal zata fafata da Crystal Palace a wasan farko na gasar Firimiya

Date:

A  ranar Juma’ar nan 05 ga Agustan shekarar da muke ciki, za’a fara gasar Firimiya ta kasar Ingila ta kakar wasannin shekarar 2022/2023 inda Arsenal da Crystal Palace zasu bude fagen gasar.

 

Filin wasa na Selhurst Park mallakin Crystal Palace ne zai karbi bakuncin fafatawar da kafin fara wasan zaá gudanar da kasai taccen biki.

 

Manchester City ce dai itace ke rike da kofin bayan lashewa da tayi sau biyu a jere a 2020/2021 da kuma 2021/2022.

 

Jadawalin wasannin makon farko na gasar sun hada da wasan…………

 

Crystal Palace da Arsenal a Ranar Juma’a 5 ga watan na Agusta.

 

Sai kuma Ranar Asabar 6 ga watan Agusta

 

Fulham da Liverpool

 

Leeds United da Wolverhampton Wanderers

 

Newcastle United da Nottingham Forest

 

Tottenham da Southampton

 

Bournemouth da Aston Villa

 

Everton da Chelsea

 

Yayin da Ranar Lahadi 7 ga watan Agusta

 

Manchester United da Brighton & Hove Albion

 

Leicester City da Brentford

Manchester City masu rike da gasar
Manchester City masu rike da gasar

West Ham United da Manchester City

 

Sai dai za a yi hutun gasar ta Firimiya a makon ranar 12 da 13, da kuma wasannin da zasu gudana a watan Nuwamba zuwa 26 ga watan Disambar.

 

Sakamkon gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da za a gudanar a kasar Qatar.

 

Kungiyoyin Fulham, da Bournemouth da Nottingham Forest sune cika makin kungiyoyi da zasu kasance 20 da zasu buga gasar ta Firimiya.

 

Bayan da Burnley, da Watford da kuma Norwich Cit suka fada gasar data gabata.

 

Wasan farko dai shine zai nuna yadda Arsenal karkashin jagorancin Mikel Arteta’s tayi shirin fara gasar.

 

Bayan siyan ‘yan wasan Manchester City biyu Gabriel Jesus da kuma Oleksandr Zinchenko, har ma da karin wasu ‘yan wasan kamar Fabio Vieira da Matt Turner da kuma Marquinhos.

 

Sai kuma Crystal Palace data sayi ‘yan wasa Cheick Doucure da Sam Johnstone da kuma Malcolm Ebiowei.

 

Haka kuma a karon farko za a fara sauyin ‘yan wasa biyar a gasar ta Firimiya, bayan tin da fari an fara hakan a manyan gasar kasashen turai biyar Bundesliga da Ligue 1 da La Liga da kuma Serie A.

Latest stories

Related stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...