Mukhtar Yahya Usman
Dan takarar gwamnan Kano a jamâiyar NNPP Abba Kabir Yusuf ya yi karar gwamnatin Kano Abdullahi Umar Ganduje a gaban kotu bisa siyar da filin wasa na mahaha da kuma katangar filin wasa na Sani Abacha dake unguwar kofar mata.
Abba Kabir ya shigar da karar ne karkashin wasu lauyoyi, inda ya zargi gwaman da cefanar da wasu kotunan musulunci biyu a nan Kano.
Sauran wadanda  ake karar sun hada da kwamishinan shariâa na jihar Kano da hukumar kasa da safayo.
Da ya ke zantawa da Premier Radio a madadin Abba Kabir Lauyansa Barista Bashir Yusuf Tudun Wuzurci ya zargi gwamnan da cefanar da wuraren ne saboda son rai da biyan bukatar kashin rai.
Ya ce gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje na wuce gona da iri wajen siyar da irin wadannan wurare masu amfani ga alâummar jihar Kano.
Baya ga wannan kuma masu karar sun yi korafi kan siyar da wasu kotunan shariâar musulunci zuwa ga wasu dai-daikun mutane ko kuma masu zaman kansu, wanda shima suke ganin hakan ya sabawa dokar kasa.
Masu karar dai sun shigar da ita ga babban  babban mai shariâa na Kano, Justice Nura Sagir, wanda kuma ya sanya ranar 10 da 11 ga  Nuwamba domin fara sauraran karar.