Karibullah Abdulhamid Namadobi
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai tafi kasar Mauritania don karbar kyautar zaman lafiya.
Mai Magana da yawun shugaban kasa Femi Adesina ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda yace shugaban kasar zai karbi kyautar saboda irin gudunmawar da yake baiwa ta fannin zaman lafiya a Afirka.
Buhari zai karbi kyautar Karfafa zaman lafiya ne a kasar
Adesina ya ce kafin karbar kyautar zaman lafiyar, Buhari zai gabatar da makala a taron Afirka kan samar da zaman lafiya.
Ya kuma kara da cewa Buhari zai bar kasar nan a yau Litinin.
A cikin tawagar da zata raka shugaban kasa Muhammadu Buhari akwai ministan harkokin wajen kasar nan, Geoffrey Onyeama da minisan Tsaro Manjo-Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya da kuma shugaban hukumar leken asiri ta kasar nan Ahmed Rufai Abubakar da sauransu.