Saurari premier Radio
31.9 C
Kano
Monday, May 6, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiBuhari zai tafi Mauritania don karbar kyautar zaman lafiya

Buhari zai tafi Mauritania don karbar kyautar zaman lafiya

Date:

Karibullah Abdulhamid Namadobi

 

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari  zai tafi kasar Mauritania don karbar kyautar zaman lafiya.

 

Mai Magana da yawun shugaban kasa Femi Adesina ne ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda yace shugaban kasar zai karbi kyautar saboda irin gudunmawar da yake baiwa ta fannin zaman lafiya a Afirka.

 

Buhari zai karbi kyautar Karfafa zaman lafiya ne a kasar

 

Adesina ya ce kafin karbar kyautar zaman lafiyar, Buhari zai gabatar da makala a taron Afirka kan samar da zaman lafiya.

 

Ya kuma kara da cewa Buhari zai bar kasar nan a yau Litinin.

 

A cikin tawagar da zata raka shugaban kasa Muhammadu Buhari akwai ministan harkokin wajen kasar nan, Geoffrey Onyeama da minisan Tsaro Manjo-Janar Bashir Salihi Magashi mai ritaya da kuma shugaban hukumar leken asiri ta kasar nan Ahmed Rufai Abubakar da sauransu.

Latest stories

Sarkin musulmi ya ja hankalin shugabanni kan samarwa da al’umma makoma

Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na 3...

Related stories

Sarkin musulmi ya ja hankalin shugabanni kan samarwa da al’umma makoma

Mai alfarma sarkin musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na 3...