Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAkwai yiwuwar kai hare-haren ta'addanci a Legas- “Yan Sanda

Akwai yiwuwar kai hare-haren ta’addanci a Legas- “Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan Legas ta sanar da cewa tana cikin shirin ko-ta-kwana bisa zargin ‘yan ta’adda za su kai hare-hare a wasu muhimman wurare a cikin jihar.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin  ne ya bayyana hakan, a wata sanarwa da ya fitar, inda ya nuna cewa suna sane da yiwuwar fuskantar wasu hare haren ta’addanci a jihar ta legas.

Sanarwar ta kara da cewa, saboda haka jami’an tsaro sun yi shiri na musamman domin maganin duk wani ko wasu da za su iya tada hankulan al’ummar jihar.

A ‘yan kwanakin nan an samu karuwar kai hare-haren ta’addanci a sasan kasar nan ciki har da babban birnin tarayya Abuja.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...