Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Sunday, April 14, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai2023: Kwankwaso zai kaddamar da Pastor a matsayin mataimakinsa

2023: Kwankwaso zai kaddamar da Pastor a matsayin mataimakinsa

Date:

Mukhtar Yahya Usman
A ranar Litinin din nan ne dan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, zai gabatar da mataimakinsa ga ‘yan kasar.

Wasu hotuna da dan takarar ya wallafa a shafinsa na Facebook sun nuna tsohon gwamnan na Jihar Kano da tawagarsa suna duba babban dakin taro na International Conference Centre da ke Abuja, inda za a gudanar da taron.

A makon jiya ne Sanata Kwankwaso ya Fasto Idahosa, dan asalin Jihar Edo da ke Kudu maso Kudancin Najeriya, a matsayin mutumin da zai yi masa mataimaki a zaben 2023.

Faston, wanda fitaccen mawakin bushara ne, ya taɓa samun lambar yabo ta Majalisar Dinkin Duniya a matsayin jakadan zaman lafiya, saboda gagarumar gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban bil adama da zaman lafiya ta hanyar wa’azinsa.

Ya fitar da kundi uku na jerin waƙoƙin bushara a baya.

Bishop Isaac Idahosa shi ne shugaba, kuma babban Fasto na cocin God First Ministry, wadda aka fi sani da Illumination Assembly, da ke Lekki Ajah, a jihar Legas.

Cocin da ya kafa sama da shekaru 25 da suka gabata.

Latest stories

Gov. Yusuf Clashes with Ganduje over Governance Failure Accusations

Karibu Abdulhamid Kano State Governor, Alhaji Abba Kabir Yusuf, and...

Related stories