Gwamnatin tarayya ta ce daga yanzu jiragen sama ne za su dinga yi wa jirgin ƙasa na Abuja zuwa Kaduna rakiya da zarar ya ci gaba da aiki.
Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ne ya bayyana hakan ranar Laraba lokacin da ya kai ziyara jihar don gane wa idonsa abin da ya faru.
Bayan ya duba waÉ—anda suka jikkata a Asibitin 44 na Sojoji a Kaduna, Amaechi ya kuma gana da Hafsan Sojojin Sama Air Marshal IO Amao da kuma Gwamna Nasir El-Rufai na Kaduna.
“Na faÉ—a wa hafsan sojan sama cewa idan muka gama gyaran layin dogo, jirgin zai ci gaba da aiki bisa rakiyar tsaro ta sama daga sojan sama har sai an saka kayayyakin tsaro daga nesa kamar yadda shugaban Ć™asa ya ba da umarni,” in ji Amaechi cikin wani saĆ™on Twitter.
Ministan ya zargi “abokan aikinsa” cewa su ne ke hana ruwa gudu tun lokacin da ma’aikatarsa ta nemi kuÉ—in sayen kyamarorin tsaron a baya