Kotun Ma’aikata ta Kasa ta umarci kungiyar malaman jami’o’i ta janye yajin aikin da take yi.
mai shari’a Polycrp Hamman ya bayar da umarnin a zaman kotun na ranar Laraba.
Mai shari’ar ya ce dole malaman makarantar su koma bakin aiki har zuwa lokacin da za a yanke hukunci kan shari’ar.
A farkon watan nan ne gwamnatin ta gurfanar da ASUU a gaban kotun kan yajin aikin da ta kwashe wata bakwai tana yi.