Tubabbun ‘yan Boko Haram 25 ne suka mutu sakamakon barkewar amai da gudawa a sansaninsu da ke Maiduguri a jihar Borno.
Rahotanni sun bayyana cewa mutane bakwai ne suka fara mutuwa a ranar Talatar da ta gabata, sai kuma wasi 14 suka mutu a ranar Laraba.
Akwai mutane fiye da dubu daya a sansanin tubabbun ‘yan Boko Haram dake karbar kulawar likitoci.
Wani jami’I a ma’aikatar lafiya ta jihar Borno da ya nemi a sakaye sunan sa ya tabbatar da faruwar lamarin.
Sai dai ya ce tubabbun ‘yan Boko Haram 11 ne cutar amai da gudawar ta kashe ba 20 ba.