Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin KanoYarbawa sun sa ke nada Ganduje sarauta

Yarbawa sun sa ke nada Ganduje sarauta

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Majalisar Malamai ta jihohin Yarbawa ta baiwa gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje sarautar Alaudden of Yoruba

Wanan na zuwa ne kwanakin biyu bayan da Alafin na Oyo ya nadashi da matarsa sarautar Aare Fiwajoye and Yeye Aare Fiwajoye na kasar Yarubawa.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da mataimakin na musamman ga gwamnan kan al’amuran daukar hoto Aminu Dahiru ya fitar ranar Talata.

Sanarwar ta nuna gwamnan ya sake samun sabuwar sarautar ne a ranar Asabar 18 ga Yuni da muke ciki.

Shugaban majalisar limamai da malamai na Jihar, Oyo Sheikh Abdulganiyyu Abubakar ne ya nada gwamnan a madadin limanan.

Da yake jawabi Sheikh Abdulganiyyu ya ce ana bayar da sarautar ne ga Musulmi mai riko da addini da kuma yi wa addinin hidima.

A cewarsu binciken su ya tabbatar musu Gwamna Ganduje ya cika wandannan sharuddan.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...