Karibullah Abdulhamid Namadobi
An kama wasu mutane 18 da ake zargi da laifin satar jama’a tare da kwace makaman da aka samu a wajensu.
Daga cikin makaman da aka kamasu dasu akwai bindiga guda daya kirar AK-47 da bindigogi kanana guda biyu da tarin alburusai.
Kakakin rundunar yan sanda na jihar Benue Catherine Anene Sewuese ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar.
Sanarwar tace mutanen da ake zargin sun yi kokarin guduwa a wani shingen bincike na ‘yan sanda dake karamar hukumar Utonkon ta jihar.
Tuni dai aka fara bincike kan wadanda ake zargi da aikin satar mutanen da aka kama da yanzu haka suke hannun yan sanda.