Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai'Yan sanda a Kano sun harbe yan ta'adda uku a Tudun Wada

‘Yan sanda a Kano sun harbe yan ta’adda uku a Tudun Wada

Date:

Rundunar ‘yan sandan Kano ta harbe masu gurkuwa da mutane 3 a karamar hukumar Tundun Wada.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da kakakin rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikowa Premier Radio ranar Lahadi.

Kiyawa ya ce a cikin daren ranar Asabar ne rundunar ta samu rahoton ‘yan bindiga sunyi garkuwa da wasu yan mata biyu, yayan mutum daya.

Yan bindigar sun shiga kauyen Katsinawa ne suka kuma sace yayan wani mai suna Elesha Aminu suka kuma gudu da su zuwa dajin Falgore.

Yan Matan su ne Zainab Elesha mai shekaru 16 da kuma Nafisa Elesha mai shekaru 18.

A cewarsa bayan samun rahoton ne kuma yan sanda tare da yan sa kai suka shiga dajin na Falgore suka kuma yi musayar wuta da yan ta’addan.

Ya yin musayar wutar rundunar ta yi nasarar kashe mutanen uku tare da kubutar da ‘yan matan da suka sace.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...