Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Saturday, April 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabarai‘Yan bindiga sun sake sako mutane 5 daga cikin fasinjojin jirgin Abuja...

‘Yan bindiga sun sake sako mutane 5 daga cikin fasinjojin jirgin Abuja zuwa Kaduna

Date:

An kara kubutar da mutane 5 daga cikin mutanen da ƴan bindiga da suka sace  a harin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna a ranar 28 ga watan Maris.

Jagoran fafutukan garin an sako mutanen Tukur Mamu ne ya tabbatar da sakin nasu a  Talatar nan.

Mutanen da aka sako sun hada Farfesa Mustapha Umar Imam wanda ke aikin jinya a asibitin koyarwa na Jami’ar Usman Dan Fodio da ke Sakkwato da Akibu Lawal da Abubakar Ahmed Rufai da Mukthar Shu’aibu da Sidi Aminu Sharif.

Kawo yanzu dai mahukuntan Najeriya ba su ce komai ba dangane da sakin mutanen.

Latest stories

Related stories