Saurari premier Radio
25.1 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiINEC ta ja kunnen mutane game da shafukan hukumar na bogi

INEC ta ja kunnen mutane game da shafukan hukumar na bogi

Date:

Hukumar zabe ta kasa INEC tayi kira ga al’umma da su kauracewa shiga komar yan damfara da sunan yi musu rajistar katin zabe.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Festus Okoye ne yayi kiran a wata sanarwa da ya fitar, yana mai tabbatar da rufe yin rajistar tun a Lahadin da ta gabata.

A cewar hukumar,  wasu marasa kishin kasa sun bude shafukan intanet na bogi da sunan hukumar, inda suke yaudarar al’umma da cewa gwamnatin tarayya ta amince da a ci gaba da yiwa jama’a rajistar, domin magance cunkoso a ofisoshin INEC.

Wannan ya biyo bayan cikar wa’adin rufe yin rajistar da INEC ta sanya.

Kafin haka dai, kungiyoyin fafutuka, sun nemi a tsawaita lokacin domin baiwa karin yan Najeriya damar mallakar katin zabe.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...