Saurari premier Radio
28.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiINEC ta ja kunnen mutane game da shafukan hukumar na bogi

INEC ta ja kunnen mutane game da shafukan hukumar na bogi

Date:

Hukumar zabe ta kasa INEC tayi kira ga al’umma da su kauracewa shiga komar yan damfara da sunan yi musu rajistar katin zabe.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar Festus Okoye ne yayi kiran a wata sanarwa da ya fitar, yana mai tabbatar da rufe yin rajistar tun a Lahadin da ta gabata.

A cewar hukumar,  wasu marasa kishin kasa sun bude shafukan intanet na bogi da sunan hukumar, inda suke yaudarar al’umma da cewa gwamnatin tarayya ta amince da a ci gaba da yiwa jama’a rajistar, domin magance cunkoso a ofisoshin INEC.

Wannan ya biyo bayan cikar wa’adin rufe yin rajistar da INEC ta sanya.

Kafin haka dai, kungiyoyin fafutuka, sun nemi a tsawaita lokacin domin baiwa karin yan Najeriya damar mallakar katin zabe.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...