Tsohon Darakta-Janar na Hukumar tsaro ta DSS, Lawal Daura, ya musanta ikirarin cewa gwamnatin tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ita ce mafi muni a tarihin kasar.
Lawal Daura ya ce kafin yanke irin wannan hukunci, ya kamata masu wannan ra’ayi su duba tarihin siyasar Najeriya daga shekarar 1995 zuwa 2023.
Ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels Television ranar Litinin.
Daura ya ce tsohon Shugaba Buhari ya dogara da wasu mutane da yake da ya amince da su, amma daga bisani wasu daga cikinsu suka ci amanar sa.
Ya ce matsaloli sun fara bayyana sosai a gwamnatin ne bayan ya bar mukaminsa na Darakta-Janar na DSS a shekarar 2018.
“Komai ya fara tabarbarewa ne bayan shekarar 2018, tun bayan da na bar mukamina,” in ji Daura.
Daura ya kuma musanta zargin cewa yana cikin wata kungiyar masu fada aji da ake kira cabal da suka dabaibaye tsohon shugaban.
Ya ce kasancewarsa shugaban hukumar leken asiri na bukatar ya kasance yana da kusanci da shugaban kasa domin gudanar da ayyukansa yadda yaTsohon Shugaban DSS Lawal Daura ya musanta cewa gwamnatin Buhari ce mafi muni a tarihin Najeriya
Tsohon Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Najeriya (DSS), Lawal Daura, ya musanta ikirarin cewa gwamnatin tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ita ce mafi muni a tarihin kasar.
Lawal Daura ya ce kafin yanke irin wannan hukunci, ya kamata masu wannan ra’ayi su duba tarihin siyasar Najeriya daga shekarar 1995 zuwa 2023.
Ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels Television ranar Litinin.
Tsohon shugaban DSS din ya ce tsohon Shugaba Buhari ya dogara da wasu mutane da yake da cikakken amincewa da su, amma daga bisani wasu daga cikinsu suka ci amanar wannan amana.
Ya ce matsaloli sun fara bayyana sosai a gwamnatin ne bayan ya bar mukaminsa na Darakta-Janar na DSS a shekarar 2018.
“Komai ya fara tabarbarewa ne bayan shekarar 2018, tun bayan da na bar mukamina,” in ji Daura.
Daura ya kuma musanta zargin cewa yana cikin wata kungiyar ‘yan fada aji da ake kira cabal a kusa da tsohon shugaban kasar.
Ya ce kasancewarsa shugaban hukumar leken asiri na bukatar ya kasance yana da kusanci da shugaban kasa domin gudanar da ayyukansa yadda ya kamata.
“Akwai ‘yan boko-boko da ke kewaye da Buhari, amma wasu daga cikinsu sun ci amanar amincewar da tsohon shugaban ya yi musu,” in ji shi.
Daura ya ce abin da ya faru a lokacin ya nuna muhimmancin duba kwarewa da cancantar mutum wajen nada shi mukamin gwamnati, ba wai dogaro da amincewar shugaban kasa da shi kadai ba.
Ya kara da cewa nada mutane bisa amincewar da shugaban kasa yake da ita gare su kadai na iya haifar da mummunan sakamako ga tafiyar da gwamnati. kamata.
“Akwai ‘yan boko-boko da ke kewaye da Buhari, amma wasu daga cikinsu sun ci amanar amincewar da tsohon shugaban ya yi musu,” in ji shi.
Daura ya ce abin da ya faru a lokacin ya nuna muhimmancin duba kwarewa da cancantar mutum wajen nada shi mukamin gwamnati, ba wai dogaro da amincewar shugaban kasa da shi kadai ba.
Ya kara da cewa nada mutane bisa amincewar da shugaban kasa yake da ita gare su kadai na iya haifar da mummunan sakamako ga tafiyar da gwamnati.
