Saurari premier Radio
34.9 C
Kano
Thursday, April 18, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiTinubu ya tafka kuskure da ya zabi Musulmi mataimaki-Babachir

Tinubu ya tafka kuskure da ya zabi Musulmi mataimaki-Babachir

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Tsohon Sakataren Gwamnatin tarayya Babachir Lawal, ya ce Bulo Ahmad Tinubu ya tafka babban kuskure wajen zabar musulmi a matsayin mataimakinsa.

Wanan na kunshe cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata ga manema labarai.

Idan za a iya tunawa dai a ranar Lahadi ne Tinubu ya zabi tsohon gwamnan jihar Borno Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a zaben da za a yi a shekara mai zuwa 2023.

Lawal ya ce zaben na Shettima ya nuna cewa wasu ‘yan baranda kuma ‘yan amshin-shata ne suka takura Tinubun ya yi haka.

Ya ce bisa ga dukkan alamu, gwamnonin arewa da wasu manyan arewar ne suka sa hakan , da cewa ba za su taba zabar dan takarar da ke da mataimaki Kirista dan arewa ba, kuma shi Tinubun ya yarda da su, in ji Babachir.

Latest stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...