Mukhtar Yahya Usman
Hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON ta ce za ta hukunta duk wanda ta kama da hannun wajen janyowa alhazai rashin zuwa kasa mai tsarki.
Wanann na cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar.
Hukumar ta kuma baiwa mamiyyatan hakuri kan rashin samun damar gudanar da aikin a bana.
Idan za a iya tunawa dai sama da maniyyata 9000 suka gaza samun zuwan kasa mai tsarki a fadin kasar nan domin gudanar da aikin hajjin bana.
Ko a nan Kano ma sai da aka tafi aka bar maniyyata kimanin 900 a kasa, wadanda basu samu damar zuwa ba.