Aminu Abdullahi Ibrahim
Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai halarci yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jamâiyar APC Bola Ahmad Tinubu a jihohi goma na kasar nan.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Kashim Shettima, kuma ministan ayyuka Festus Keyamo, ya fitar a jiya Jumaâa.
Ya ce Buhari ya amince da halartar yakin neman zaben Bola Ahmad Tinubu, da za ayi a jihohi goma na kasar nan da suka hada da Yobe da Sokoto da Adamawa da dai sauransu.
A watan Nuwambar bara ne dai shugaba Buhari ya halarci yakin neman zaben Bola Ahmad Tinubu da akayi a Jos dake jihar Plateau, bayan ya amince ya zama shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jamâiyar APC.