Saurari premier Radio
23.8 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiShugaba Buhari zai taya Bola Tinubu yakin neman zabe

Shugaba Buhari zai taya Bola Tinubu yakin neman zabe

Date:

Aminu Abdullahi Ibrahim

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai halarci yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyar APC Bola Ahmad Tinubu a jihohi goma na kasar nan.

 

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu da Kashim Shettima, kuma ministan ayyuka Festus Keyamo, ya fitar a jiya Juma’a.

 

Ya ce Buhari ya amince da halartar yakin neman zaben Bola Ahmad Tinubu, da za ayi a jihohi goma na kasar nan da suka hada da Yobe da Sokoto da Adamawa da dai sauransu.

 

A watan Nuwambar bara ne dai shugaba Buhari ya halarci yakin neman zaben Bola Ahmad Tinubu da akayi a Jos dake jihar Plateau, bayan ya amince ya zama shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyar APC.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...