Babban sufeton ƴan sandan kasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun yace ƴan sanda ba za su lamunci duk wani abu da zai kawo rikici ba yayin zanga-zangar da gamayyar kungiyoyin kwadago ta kasa NLC zata gabatar a gobe Laraba.
Sanarwar da kakakin rundunar ƴan sandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar ta ce ƴan ƙasa suna da ƴancin yin zanga-zanga kamar yadda kundin mulki ya tanada amma dole ne a gudanar da ita cikin kwanciyar hankali.
Rundunar ƴan sandan ta ce a baya irin wannan zanga-zanga tana rikiɗewa ta zama tashin hankali, saboda haka ta ke gargaɗin cewa ba za ta bari a gudanar da duk wani abu da zai kawo matsalar tsaro ba.
ACP Adejobi ya ce duk wani yunƙurin tayar da rikici a lokacin zanga-zangar ƙungiyar ƙwadago zai fuskanci fushin hukuma.
Ƙungiyoyin ƙwadago a kasarnan sun shirya fara zanga-zanga a faɗin ƙasar daga ranar Laraba 2 ga watan Agusta domin nuna rashin amincewa da soke tallafin manfetur da gwamnatin tarayya tayi.