Saurari premier Radio
37.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiRundunar sojin kasar nan ta musanta sace mutane a hanyar Damaturu

Rundunar sojin kasar nan ta musanta sace mutane a hanyar Damaturu

Date:

Rundunar Sojin-ƙasar nan ta musanta raɗe-raɗin da a ke yi cewa an yi garkuwa da matafiya a kan titin Maiduguri-Damaturu  da yamamcin ranar Asabar.

Premier Radio ta ruwaito kakakin rundunar haɗin gwiwa ta 7 ‘Operation Haɗin Kai’ Ado Isa ne ya musanta hakan cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce zantuttukan da ake yadawa basu da tushe ballantana makama, a don hakan ne ya nemi jama’a da suyi watsi da shi.

“Mun samu rahoton raɗe-raɗin da a ke yaɗawa a kafafen sadarwa ranar Asabar.

“Haka kuma wasu jaridu ma sun buga jita-jitar cewa wai ISWAP sun yi garkuwa da matafiya a Borgozo a Ƙaramar Hukumar Kaga a Borno.

“To wannan jita-jitar ba ta da tushe kuma ana yaɗa ta ne  domin a kushe ƙoƙarin da “Operation Hadin Kai’ ke yi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƴan Boko Haram ne su ka yi yunƙurin tare hanya a yankin Dole/Bari domin su tada hankalin al’umma.

“Dakarun da ke sintiri a wurin ne su ka zo su ka daƙile yunƙurin na su.

“Ba a ɗauke wani matafiyi a ranar Asabar ba, kawai dai aikin ɓatagari da su ke baƙin ciki cewa zaman lafiya na dawowa a arewa-maso-gabas,’ in ji shi.

Ya kuma jaddada ƙoƙarin da rundunar ke yi na kare  matafiya a titin.

Latest stories

Related stories