Hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA ta ce da dawo da yan ciranin kasar 175 da suka makale a Libiya.
NEMA ta ce cikin wadanda aka dawo da su din akwai mata 81 da kuma maza 94.
A cewrta ungiyar kula da yan ci rani ta duniya da hadin gwiwar kungiyar tarayyar Turai ne suka dauki nauyin dawo da su.
A shekarun baya-bayan nan dai ‘yan kasar nan na kasadar jefa rayuwarsu cikin hatsari a kokarinsu na ficewa zuwa kasashen Turai, domin neman rayuwa mai inganci.
To amma mafi yawancinsu ba sa samun nasarar cimma muradunsu, a maimakon haka sukan makale a kasashe irinsu Libya su kuma fada hannun bata- gari inda suke shiga mawuyacin hali.
Hukumar NEMA ta ce a Janairun 2022, ta karbi ‘yan ci-rani kusan 2000 da suka komo daga Libya.