Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiBa zamu iya kawo karshen matsalar harkokin jirgin sama a kasar nan...

Ba zamu iya kawo karshen matsalar harkokin jirgin sama a kasar nan ba-Hadi Sirika

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Ministan sufurin jiragen sama na kasa Hadi Sirika, ya ce za a ba za a iya kowa karshen matsalolin da harkar sufurin jiragen sama ke fuskantaa kasar nan ba.

Hadi Sirika ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da kugiyar masu harkar sufuri a kasar nan.

Ya ce matsalalolin da bangaren sufurin jiragen sama ke fuskanta a kasar nan, sun sha kan ma’aikatarsa.

Ya ce wannan ba matsala ce da za a kawo karshenta cikin kankanin lokaci ba, saboda matsala ce ta duniya baki daya, ba Najeriya kadai ba.

Matsalar makamashi matsala ce da ta addabi duniya baki daya.

“A cewarsa yanzu haka akwai matsalar tsadar man jirgi a kasashe kama daga Amurka har zuwa New Zealand.

“Amma matsalar ta fi kamari a Najeriya saboda ba ma sarrafa shi a kasarmu, sannan ga tashin farashin Dala” In ji Ministan

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...