33.9 C
Kano
Sunday, June 4, 2023
HomeLabaraiMatasa biyar sun mutu yayin hakar kasa a Kano

Matasa biyar sun mutu yayin hakar kasa a Kano

Date:

Related stories

Maniyyata 17,000 ne suka bar Najeriya zuwa kasa maitsarki-NAHCON

Bayan kwashe kwanaki bakwai da fara jigilar alhazan Najeriya...

Wasu matasa biyar sun rasa ransu yayin da suke hakar kasa a wani rami dake kauyen Dan Lami a karamar hukumar Bichi a nan Kano.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai Magana da yawun hukumar kashe gobara Saminu Yusuf Abdullahi ya fitar a Lahadin nan.

Ya ce matasan sun mutu ne a Asabar din da ta gabata bayan da kasa ta rufto musu tare da rufesu wanda hakan yayi sanadiyyar ajalin su.

Matasan da suka rasu sun hada da Alasan Abdulhamid dan shekara 22 da Muhd Sulaiman mai shekaru 35 sai Masa’udu Nasiru dan shekara 25.

Sauran sune Jibrin Musa dan shekara 30 da kuma Jafaru Abdulwahabu shima mai shekaru 30.

Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce tuni suka mika gawarwakin su ga hukumar ‘yan sanda.

Latest stories