Majalisar dokokin Kano ta amince da karatun farko na kirkirar masarautu masu daraja ta biyu a jihar Kano.
Majalisar ta amince da wannan bukata ne a zamanta na Juma’ar nan karkashin Kakakinta Jibril Isma’il Falgore.
Amincewa da kudurin samar da masarautu masu daraja ta biyun ya biyo bayan rushe masarautu masu daraja ta daya da majalisar tayi a jiya Alhamis.
Wanda ya hakan ya kai ga dawo da Sarki Sunusi kan karagar mulkin Kano a matsayin Sarki Mai daraja ta daya.