Wasu lauyoyi 20 sun nuna sha’awarsu ta ba Abba Kyari kariya a ƙarar da Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta shigar da shi.
NDLEA dai tana zargin Abba Kyari, dakataccen Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda da hannu a cikin wata hadahadar hodar iblis.
Wani lauya, Musa Shafiu ne ya bayyana wa manema labarai haka a yau Laraba madadin sauran lauyoyin.
Musa ya ce tawagar lauyoyin ta ƙunshi lauyoyi masu muƙamin SAN har guda huɗu.
Ya ce sun yanke shawarar kare Abba Kyari ne sakamakon sadaukarwa da ya bayar a bangaren tsaro a faɗin ƙasar nan.