Tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bude makarantar koyar da ilimin shugabanci, wadda ya gina a nan Kano.
Kwankwaso ya bude cibiyar ranar Asabar, a wani bangare na bikin cikarsa shekaru 66 da haihuwa.
A ranar juma’ar da tla gabata ma ya bude masallacin juma’a a gidansa dake Bompai a Kano.
Wannan dai na cikin al’adar Kwankwaso samar da wani abu da jam’a za su amfana a duk lokacin da yake bikin ranar haihuwa