Kwamishinan ilimi na jihar Kano Umar Haruna Doguwa ne ya bayyana hakan a cikin shirin BBC na ‘A Fada A Cika,’ da aka gudanar a Kano.
Ya bayyana cewa, wani muhimmin al’amari na shirin nasu na sake fasalin ilimi shi ne gyaran ajujuwa 99 a duk shekara.
Bugu da kari, ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bada umarnin gina gidajen malamai a makarantun firamare dake fadin Kano.