Saurari premier Radio
27.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKwale-kwale ya kife da mutane 9 a Madobi

Kwale-kwale ya kife da mutane 9 a Madobi

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Ana fargabar mutane shida sun mutu bayan da wani kwale-kwale ya kife da su a garin Kanwa da ke karamar hukumar Madobi.

 

Al’amarin ya faru ne cikin daren Larabar nan a lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa gida daga garin Kura.

 

A cewar shaidun gani da ido an samu nasar tsamo mutune uku da ransu, ya yin da ake ci gaban da neman ragowar shidan.

 

Dayyabu Muhammad guda ne cikin wadanda suka rasa iyalansu a hadarin, ya ce ya rasa matarsa da ‘yan yansa maza biyu.

 

Ya ce sun rabu da matar ne za ta je gaishe da iyayenta sai labari aka bashi cewa kwale-kwalen ya kife da su.

 

“Mun rabu da ita za ta tafi gaida iyayenta, da ‘ya ‘yana biyu sai labari aka bani kwale-kwale ya kife da su.

 

“Mun je wajen munyi ta bincike a mma har gari ya waye ba mu samo su ba yanzu dai mun zubawa sarautar Allah Ido.” A cewarsa.

 

Da yake jawabi dangane da iftilain Lawan Yahya a madadin shugaban karamar hukumar Madobi ya ce wannan ibtil’ine babba.

 

Shugaban wanda ya ce  hadarin iftila’i ne mai tada hankali, inda ya bukacesu su mai da komai ga Allah madaukaki.

 

Lawan Yahya ya bukaci da su dinga kaucewa shiga ruwan musamman a wannan lokaci da ake fama da Ambaliyar ruwa.

 

Har yanzu dai ba a kai ga samo gawarwakin wadanda ake fargabar sun mutu ba.

 

Latest stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...