Ana zargin Abduljabbar Kabara ne dai da laifin yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) da kuma tayar da hankalin jama’a.
Dayake gabatar da bukatar belin, lauyan malamin ya yi wa kotu alkawarin cewa za su bi dukkanin sharuddan da za a gindaya musu.
Sai dai lauyoyin masu shigar da kara karkashin jagorancin Barista Saida Suraj sun nemi kotu ta yi watsi da bukatar bisa la’akari da girman laifin da ake tuhumar wanda ake zargi, wanda a cewarsu zai iya kai ga yanke mishi hukuncin kisa, karkashin dokar Kundin laifufuka ta Jihar Kano ACJL 171 (1).
Hakan ya sa alkalin kotun, Mai Shari’a Abdullahi Sani Sarki Yola ya dage zaman da mako biyu, zuwa ranar 31 ga watan Maris don jin ra’ayin kotun game da batun bayar da belin