Karibullah Abdulhamid Namadobi
Kotu ta keta belin da ta bayar na tsohon kwamishinan ayyuka na jihar Kano Injiniya Mu’azu Magaji Dansarauniya.
Kotu ta keta belin ne bisa abinda tace na gaza bayyanar tshohon kwamishinan da ake zargi da bata sunan gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje a gaban kotu.
Kotun tace Dansarauniya baije zaman kotu ba har sau 3, a shari’ar da ake masa.