Aminu Abdullahi Ibrahim
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano, KEDCO ya baiwa al’umma a Kano da Jigawa hakuri na karancin wutar lantarki da a ke samu a ƴan kwanakin nan.
A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Kamfanin, Ibrahim Sani Shawai ya fitar, ya ce matsalar ta afku ne sakamakon raguwar adadin wutar da kanfanin tunkudu wutar lantarki na kasa TCN ya yi a kwanakin nan
Ya ce ita ma hukumar ta TCN ta fuskanci ƙarancin wutar ne sakamakon ƙarancin wutar da ga Kamfanonin da su ke samar da ita wato ‘Generation Companies’ zuwa ga KEDCO.
Ya ce an fi samun ƙarancin wutar da ga ƙarfe 6 na yamma da kuma 11 na dare.
Bayan da ya baiwa al’umma haƙuri, Shawai ya tabbatar da cewa za a shawo kan lamarin nan ba da daɗewa ba.