Bayan da gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 ke ci gaba da gudana a kasar Qatar, tuni a wannan rana wasanni zasu ci gaba da gudana.
Lamarin da ke nuni da wasanni zagaye na kasashe 16 za a ci gaba da fafawa, bayan kammala wasanni rukuni.
Jumulla dai kasashe 32 ne suka fafata gasar, da kuma kasa daya ce Zata zama zakara a wasan karshe da zai gudana a filin wasa na Lusail a ranar 18 ga Disambar da muke ciki.
Sai dai abu mafi kayatarwa da Kuma burgewa shi ne, kasashe biyu cikin biyar a nahiyar Afrika da suka halarci wannan gasa, sune kawai suka samu damar kaiwa ga zagaye na kasashe 16.
Wato Morocco da ta kammala a mataki na farko a rukunin D da maki 7, sai kuma Senegal wadda ta kammala da maki 6 a rukunin A na wannan gasa…
Cikin wasannin da zasu gudana bari mu fara da wasan farko na zagayen kasashe 16 da za ai gumurzu a Asabar dinnan 3 ga Disamba…
Netherlands da Amurka a filin wasa na Khalifa International Stadium da karfe 4 na yamma.
Sai Argentina da Australia a filin wasa na Ahmad Bin Ali Stadium da karfe 8 na dare.
A ranar Lahadi 4 ga Disamba kuwa….
France da Poland a filin Al Thumama Stadium da karfe 4 na yamma.
Yayin da England da Senegal a filin wasa na Al Bayt Stadium da karfe 8 na dare.
A ranar Litinin 4 ga wata kuwa..
Japan zata kece raini da Croatia a filin Al Janoub Stadium da karfe 4 na yammaci.
Sai kasa Mafi lashe wannan gasa Brazil zata buga da Koriya ta Kudu a filin Stadium 974 da karfe 8 na dare.
Haka zalika a ranar Talata 5 ga watan na Disamba kuwa..
Morocco da kasar Spain a filin wasa na Education City, wasan da zai gudana da karfe 4 na yammacin ranar.
Sai kuma Portugal da Switzerland a filin wasa na Lusail Stadium, da karfe 8 na daren ranar.
1_Netherlands
2- Amurka
3-Argentina
4-Australia
5-Japan
6-Croatia
7-Brazil
8- Koriya ta Kudu
9-England
10-Senegal
11-France
12- Poland
13-Morocco
14- Spain
15-Portugal
16-Switzerland