Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Wednesday, April 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiJam'iyyar ADP ta sayar da Ibrahim Sabo dan takarar gwamna a Jigawa

Jam’iyyar ADP ta sayar da Ibrahim Sabo dan takarar gwamna a Jigawa

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Jam’iyyarADP mai alamar littafi ta tsayar da Alhaji Ibrahim Sulaiman Sabo, a matsayin ɗan takarar gwamna a jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne biyo bayan taron ƙaddamar da takarar tasa, wanda aka gudanar a Alhamis ɗinnan, a helkwatar jam’iyyar dake Dutse babban birnin jihar Jigawa.

Jam’iyyar ta zabi Sabo ne ta hanyar masalaha, inda delegate 16 suka amince da zabin.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ayyana takarar tasa, Alhaji Sabo, wanda haifaffen ƙaramar hukumar Taura ne, yace ya shirya tsaf domin ceto al’ummar Jigawa daga ƙangin da manyan jam’iyyun kasarnan na APC da PDP suka jefasu.

Yace sabuwar dokar zabe da gwamnatin APC ta kawo, ta basu cikkaken gwarin gwiwar samun nasara.

“Lokacin PDP, Jonathan ne ke kan mulki, da Allah ya ƙaddara zuwan ƙarshensa, sai ya kawo Card Reader, wanda shine yayi silar faduwarsa. To itama gwamnatin APC da ta kawo dokar zabe, matukar za’abi ƙa’ida, to ta kada kanta.”

Alhaji Sabo ya ƙara da cewa idan suka kafa gwamnati, zasu baiwa bangaren noma fifiko, zuwa fannin lafiya da ilimi da kuma tattalin arziki.

“Bangaren noma, ina tabbatar maka cewa mudai nan a Arewa, mun rike noma, kuma rabon taki da ake, nima manomi ne amma ban taba samu ba, wannan ba ƙa’ida bace. Kamata yayi a tura wakilai ko ina, a gano gonarka hekta nawa ce, kuma buhu nawa ne zai isheka.”

“Na biyu bangaren lafiya, zan tabbatar cewa in Allah ya yarda, mutum yayi haɗari ya karye ko wani abu ya faru, ba zamu bari ya zauna babu kulawar lafiya ba, har yazo ya mutu.” Inji Alhaji Sabo.

Ya kara da cewa “idan kaba mutum wadataccen abinci da lafiya da ilimi ka gama masa komai.”

Tun daga 6 ga watan Yunin da muke ciki ne jam’iyyar ta ADP ta fitar da yan takarar majalisar jiha 30 ta hanyar masalaha, sannan a 7 ga wata, ta zabi yan takarar majalisar wakilai ta tarayya 11, har ila yau ta kaddamar da masu takarar Sanata gida 3, dukkaninsu ta hanyar masalaha.

Shugaban jam’iyyar na jihar Jigawa, Comrade Bua Abdul Azeez, yace sun zabi fitar da yan takarar ta hanyar masalaha ce bisa amincewar yayan jam’iyyar.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa duk da jam’iyyar tasu ƙarama ce, zatayi nasara, kasancewar dukkanin manyan jam’iyyun sun gaza.

An gudanar da taron ƙaddamar da takarar ce gaban idanun wakilan hukumar zabe INEC, da jami’an yan sanda.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...