Ahmad Hamisu Gwale
Rukunin farko na Mahajjatan Kano 259 sun dawo Kano daga kasa mai tsarki bayan sauke faralin a bana.
Mahajjatan kanan hukumomin Rano, Bunkure da Kura ne dai jirgin farko da hukumar jin dadin alhazai ta kasa tayi jigilar su zuwa nan Kano a ranar Juma’ar nan.
Alhazan da suka hau jirgin AZMAN mai lamba ZQ2349 sun isa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da misalin karfe 02:41 na rana.
Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Muhammed Abba-Danbatta ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Muhammad Abba Danbatta ya ce alhazan sun kasance masu biyayya da bin doka a kasa mai tsarki.
Ya ce ana sa ran dawowar kashi na biyu na maniyyata nan gaba kadan.