Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin tarayya ta yi wa kungiyar  ASUU kishiya

Gwamnatin tarayya ta yi wa kungiyar  ASUU kishiya

Date:

Ministan kwadago da samar da aikin yi na kasa, Chris Ngige ya bayar da takardar shaida ga kungiyar ma’aikatan koyarwa ta jami’o’in kasar nan, wadda kungiya ce ta malaman jami’o’in tarayya da na jihohi.

Kungiyar mai suna CONUA  ana ganin kai tsaye za ta kasance kishiya ga babbar kungiyar malaman jami’ioin gwamnatin kasar nan.

Andai  kafa kungiyar CONUA ne a shekara ta 2018 a jami’ar jihar Osun.

 

Kungiyar ASUU da gwamnatin kasar nan na kai ruwa rana a dalilin  yajin aikin sai-baba-ta-gani da malaman jami’o’in suka shiga tsawon wata takwas ke nan, suna neman sai lallai gwamnati ta biya musu bukatunsu.

 

Duk da wani kokari da ban-baki da tattaunawa daga gwamnati sun kasa shawo kan kungiyar malaman kungiyar ASUU domin dakatar da yajin aiki.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...