Saurari premier Radio
25.1 C
Kano
Saturday, July 27, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamantin Kano ta samar da sabbin kotunan musulunci 3

Gwamantin Kano ta samar da sabbin kotunan musulunci 3

Date:

Gwamantin Kano ta samar da sabbin kotunan musulunci uku a wani bangare na rage cunkosu a kotunan Kano.

 

Wannan na zuwa ne bayan cece-kucen da aka samu kwanakin baya game da sauyawa wasu kotunan addinin musulunci matsuguni.

 

Kakakin manyan kotunan shari’ar musulunci na Kano, Muzammil Ado Fagge, ne ya sanar da samar da sabbin kotunan ranar Litinin.

 

Ya ce samar da karin, da ma wadanda ake da su a baya za su rage cunkuson da ake samu, tare da taimakawa gudanar da shari’a cikin sauri.

 

Muzammil Fagge, ya kuma yaba jajircewar Alkalin-Alkalai, Tijjani Yusuf Yakasai, da magatakardar kotuna, Barista Abubakar Haruna Khalil, wajen tabbatar da samar da wadannan sababbin kotuna.

 

Kwanakin baya dai an zargi gwamnatin Kano da laifin sayar da harabar wasu kotunan shari’ar musulunci al’amarin da Kwamishinan sharia, Musa Abdullahi Lawan ya musanta.

Latest stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...

Related stories

246943801721751646

246943801721751646

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA AMURKA.

SANARWAR JANYEWA DAGA TAKARA DAGA SHUGABA JOE BIDEN NA...