Ashiru Umar
Gwaman Kano Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da wurin da bene mai hawa uku ya rikito a kasuwar waya ta Beruit wuri ajiye ababen hawa.
Wannan na zuwa ne jim Kadan bayan da gwamnan ya ziyarci kasuwar domin jajantawa wadanda al’amarin ya shafa ranar Laraba.
Ganduje ya ce tuni gwamnati ta kafa kwamiti na musamman da zai binciki matsalar domin daukar matakin da ya da ce.
Gwamnan ya kuma bukaci al’ummar kasuwar da su baiwa gwamnati hadin kai yayin gudanar da binciken.
Ganduje ya bayyana cewa daga yanzu gwamnati ta mayar da inda abin ya faru wurin ajiye ababan hawa.
A na sa jawabin shugaban masu saida wayoyi na kasa Alhaji Musa Haruna ya ce ´yan kasuwar sun girgiza bayan da suka tsinkayi zaftarowar ginin babu tsamani.
Ya ce amma sun godewa Allah da ba a samu asarar rayuka da yawa ba.
Musa Hashim ya kuma godewa gwamnatin Kano dangane da matakin da ta dauka.
A jiya ne dai wani bene da ake ginawa mai hawa uku ya rikito a kasuwar inda ya hallaka mutum guda tare da jikkata wasu da dama.